Isa ga babban shafi
Tarayyar Turai

EU ta amince da sake matsuguni ga bakin haure

Shugabannin Kungiyar kasashen Turai sun amince su sake matsuguni ga dubban baki 'yan ci rani da suka isa kasahsen Italiya da Girka a wani taro da suka yi daren jiya.

Daya daga cikin bakin hauren dake nuna cewa ba za su koma kasashen su ba
Daya daga cikin bakin hauren dake nuna cewa ba za su koma kasashen su ba REUTERS/Eric Gaillard
Talla

Shugaban taron Donald Tusk ya ce, za’a rarraba bakin haure dubu 40 zuwa wasu kasashen dake kungiyar a cikin shekaru biyu masu zuwa amma ba tare da sanya sharadi kan adadin da kowacce kasa za ta karba ba.

Sabbin alkaluman Majalisar Dinkin Duniya sun nuna cewa bakin haure dubu 63 ne suka isa Girka ta ruwa a cikin wanna shekarar yayin da dubu 62 suka isa Italiya banda dubban da suka mutu.

Akasarin bakin hauren sun baro kasashensu ne saboda tashe tashwn hankula da kuma matsalar talauci.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.