Cameron ya amsa fallasar Panama
Firaministan Birataniya David Cameron ya ce ko shakka babu ya taba amfana da kudaden da ake cewa mahaifinsa ya mallaka a kasashen ketare kamar dai yadda bayanan sirri na Panama da aka fallasa suka ambaci sunansa.
Wallafawa ranar:
Bayan share tsawon kwanaki hudu ba tare da ya ce uffan a game da wannan zargi ba, daga bisani Cameron ya tabbatar da cewa ya gaji hannayen jari wadanda ya sayar a shekara ta 2010 da kimarsu ta kai Euro dubu 40.
Zargin rashawa ko kuma boye kudade a kasashen ketare, ya shafi shugabannin kasashen duniya da dama da suka hada da Mauricio Macri na Argentina, da shugaban Rasha vladimir Putin har ma da shugaban China Xi Jinping da dai sauransu.
A halin yanzu dai Shugaban Argentina na fuskantar bincike a game da zargin rashawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu