Isa ga babban shafi
Jamus

wani matashi ne dan kasar Iran ya kai harin Munich na kasar Jamus

Akalla mutane 9 ne suka rasa rayukansu bayan wani dan bindiga ya kai hari a wani katafaren shagon siyar kayayyakin masarufi da ke birin Munich na kasar Jamus.

wasu jamian tsaron kasar Jamus kenan a kusa da shagon da aka kai harin na daren jumaa 22 zuwa 23  ga watan yuli  2016.
wasu jamian tsaron kasar Jamus kenan a kusa da shagon da aka kai harin na daren jumaa 22 zuwa 23 ga watan yuli 2016. REUTERS/Michael Dalder
Talla

Jami’an ‘yan sandan Jamus sun bayyana cewa, wani matashi ne dan kasar jamus dan asalin kasar Iran mai shekaru 18 a duniya ne, ya kai harin na jiya jumma’a.

Jaridar Bild ta Jamus ta rawaito cewa, an hangi maharin na bude wuta ba tare da kakkautawa ba a cikin katafaren shagaon saida kayyakin masarufin da ke kusa da wani filin wasannin Olympics kafin daga bisani ya ruga ta hanyar wata tashar jirgin kasa.

Tun lokacin da wani matashi dan kasar Afhanistan ya kai harin wuka kan fasinjojin wani jirgin kasa a Bavaria a ranar Litinin da ta gabata, jami’an tsaron Jamus ke cikin shirin ko-ta-kwana.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.