Isa ga babban shafi
Colombia

'Yan tawayen FARC sun mika sojoji yara ga gwamnatin Colombia

Kungiyar ‘Yan tawayen FARC ta kasar Columbia, ta mika tawagar farko ta sojoji kananan yara ga gwamnatin kasar, a matsayin fara cika alkawarin da ta dauka bayan cimma yarjejeniyar ajiye makamai tsakaninta da gwamnati. 

'Yan tawayen FARC na Colombia da suka ajiye makamai a watan da ya gabata
'Yan tawayen FARC na Colombia da suka ajiye makamai a watan da ya gabata REUTERS/File
Talla

Kungiyar bada agaji ta Red Cross ta ce za’a fara tura yaran guda takwas asibiti, domin duba lafiyarsu kafin mika su ga iyalansu, daga bisani kuma a tura su zuwa cibiyar da gwamnatin kasar ta tanada domin gyaran halayya.

‘Yan tawayen na FARC da suka ajiye makami a watan da ya gabata, sun ce akwai yara da aka tilastawa shiga aikin soja 21 a karkashinsu, kuma tun a waccan lokacin suka yi alkawarin mika su ga gwamnati.
 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.