EU ta shatawa Burtaniya sharuda masu tsauri
Kungiyar kasashen Turai ta bukaci Burtaniya ta kai wani minzali a shirinta na ficewa daga EU kafin ta bijiro da batun tattaunawar yarjejeniyar kasuwanci da kungiyar.
Wallafawa ranar:
Shugaban tarayyar Turai, Donald Tusk ya yi watsi da bukatar Burtaniya ta shiga tattaunawar huldar kasuwanci da EU a dai dai lokacin da ta fara shirin aiwatar da shirn ficewarta baki daya.
Mista Tusk, ya ce, mambobin kasashen Turai 27 za su kulla yarjejeniyar ce bayan Burtaniyar ta kamala ficewa baki daya a shekara ta 2019, a karkashin tsauraran ka’idojin.
Sai dai ya ce, ba wai za su kuntata wa mata ba ne, saboda ficewarta ka dai ya isheta damuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu