Isa ga babban shafi
Faransa-Birtaniya

Macron zai kawo cikas a ficewar Birtaniya- 'Yan adawa

Masu adawa da kungiyar kasashen Turai sun mayar da zazzafan martani game da zaben Emmanuel Macron a matsayin sabon shugaban Faransa, in da suka bayyana nasararsa da mummunan labari da ka iya haifar da cikas dangane da tattaunawar ficewar Birtaniya daga kungiyar kasashen Turai.

Zababben shugaban Faransa Emmanuel Macron na kyamar ficewar Birtaniya daga kungiyar kasashen Turai
Zababben shugaban Faransa Emmanuel Macron na kyamar ficewar Birtaniya daga kungiyar kasashen Turai REUTERS
Talla

A wannan Litinin, dan gani-kashenin ficewar Birtaniya daga kungiyar Turai Nigel Farage ya ce, shugaban hukumar kungiyar Turai Jean Claude Juncker, zai juya Emmanuel Macron yadda ya ke so a tattaunawar ficewar Birtaniya daga kungiyar.

Kungiyar da ke kyamar hadin kan kasashen Turai ta Birtaniya ta bayyana nasarar Macron mai shekarau 39 tamkar mika wuya ga ‘yan Nazi na Jamus.

Jaridar Telegraph da ake wallafawa a Birtaniya ta ce, akwai yiwuwar Mr. Macron ya ci gaba da aiki da zazzafan kudirin Faransa kan ficewar Birtaniya daga kasashen Turai.

Ita ma Jaridar Daily Mail wadda ta goyi bayan kada kuri’ar ficewar Birtaniya a bara, ta rawaito wani marubuci mai suna Robert Hardman da ke bayyana Macron a matsayin mai nuna banbbanci kan ficewar.

A lokacin yakin neman zabensa, Mr. Macron ya kyamaci kuri’ar da Birtaniya ta kada don raba dari da EU, yayin da ya bayyana hakan a matsayin babban laifi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.