Isa ga babban shafi
Rasha

IAEA ta yabawa Rasha na lalata makamanta masu guba

Hukumar da ke yaki da yaduwar makamai masu guba ta duniya, IAEA, ta yabawa Rasha saboda daukar matakin lalata makaman ta masu guba, inda ta bayyana shi a matsayin gagarumar ci gaba wajen raba duniya da makaman.

Shugaban Rasha Vladimir Putin ya ce kasar ta lalata sauran makaman ta masu guba
Shugaban Rasha Vladimir Putin ya ce kasar ta lalata sauran makaman ta masu guba Sputnik/Mikhail Klimentyev/Kremlin via REUTERS
Talla

Shugaban hukumar Ahmet Uzumcu ya kuma yabawa kasar wajen bai wa jami’an sa damar sanya ido domin lalata makaman wanda Rasha ta ce suna iya hallaka duk wani hallita da ke doran kasa.

Kasashen Rasha da Amurka sun mallaki tarin makamai masu guba wanda suka ce zasu lalata bayan sanya hannu kan yarjejeniyar kauda makaman a shekarar 2012.

Sai dai Rashan ta zargi Amurka da kin lalata nata makaman.

Rasha da ta gaji tarin wadannan makamai masu guba daga Tarayyar Soviet, Shugabanta Vladimir Putin ya ce matakin wani yunkurin ne na tabbatar da zaman lafiya a fadin duniya a cikin wannan karni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.