Faransa ta buƙaci Isra'ila ta daina gine-gine a yankin Falasɗinawa
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya buƙaci Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da ya daina gine-gine a yankunan Falasɗinawa da kuma ƙaddamar da tattaunawa domin kawo zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.
Wallafawa ranar:
Yayin da yake jawabi bayan ganawar da suka yi a birnin Paris, shugaba Macron ya ce daina gine-gine zai bai wa Falasɗinawan ƙwarin gwuiwar tattaunawa da gwamnati.
Shugaba Macron na daga cikin na gaba-gaba wajen bayyana adawa da shirin Amurka na tabbatar da birnin Ƙudus a matsayin babban birnin Israila da kuma kiran taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cikin gaggawa wanda ya yi Allah-wadai da matakin.
Yanzu haka Netanyahu na ziyara a Turai, inda zai gana da ministocin harkokin waje na ƙasashen yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu