Isa ga babban shafi
Faransa

Za mu kawo karshen zanga-zanga a Faransa

Shugaban Faransa Emmanuel Macron dake jawabi a taron Argentina taron kasashe 20 masu karfin tattalin arziki na duniya ya bayyana cewa ba zai amince a ci gaba da tayar da tarzoma a kasar Faransa.

Zanga-zangar Faransa
Zanga-zangar Faransa REUTERS/Benoit Tessier
Talla

Shugaba Macron na jawabi ne a dai-dai lokacin masu zanga-zanga ke ci gaba da karo da jami’an tsaro a birnin Paris da wasu sassan kasar na Faransa.

Fadar Firaministan kasar ta sanar da cewa yan sanda suna tsare da masu zanga-zanga kusan 500,yayinda aka bayyana cewa wasu yan Sanda sun samu rauni.

Firaminista Edouard Philippe ya bukaci ganawa da wakilan masu bore,sai da hakan ya citura

Shugaba Macron a fusace ya nuna matukar damuwa tareda jadadda cewa doka zata yi aiki domin tabbatar da doka da oda a ilahirin kasar ta Faransa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.