Dan ta'addan da ya hallaka Masallata 49 ya gurfana a gaban kotu
Jami’an tsaron New Zealand sun gurfanar da dan ta'addan da ya bude wuta kan Masu Ibada a wasu Masallatan Juma’a biyu da ke birnin Christ-church a gaban kotu, bayan da ranar Juma'a ya hallaka Masallata 49 tare da jikkata wasu adadi mai yawa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
An gurfanar da dan bindigar Brenton Harrison, dan kasar Australia mai shekaru 28 a gaban babbar kotu da ke birnin na Christchurch a yau Asabar, wadda ta bada umarnin a ci gaba da tsare shi, zuwa 5 ga watan Afrilu, lokacin zamanta na biyu a kan ta’addancin da yayi.
Harin ta’addancin na ranar Juma’a dai ya sa Fira Ministar New Zealand Jacinda Ardern shan alwashin sake tsaurara dokokin mallakar bindiga a kasar, tun bayan makamancin matakin da gwamnatin kasar ta taba dauka a shekarar 1992, lokacin da wani dan bindiga ya hallaka mutane 13 ta hanyar bude musu wuta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu