Isa ga babban shafi
New Zealand

Dan ta'addan da ya hallaka Masallata 49 ya gurfana a gaban kotu

Jami’an tsaron New Zealand sun gurfanar da dan ta'addan da ya bude wuta kan Masu Ibada a wasu Masallatan Juma’a biyu da ke birnin Christ-church a gaban kotu, bayan da ranar Juma'a ya hallaka Masallata 49 tare da jikkata wasu adadi mai yawa.

Brenton Tarrant dan bindigar da ya hallaka Masallata 49 a wasu Masallatan Juma'a 2 da ke New Zealand, a tsakiyar jami'an tsaro.
Brenton Tarrant dan bindigar da ya hallaka Masallata 49 a wasu Masallatan Juma'a 2 da ke New Zealand, a tsakiyar jami'an tsaro. Mark Mitchell/New Zealand Herald/Pool/REUTERS.
Talla

An gurfanar da dan bindigar Brenton Harrison, dan kasar Australia mai shekaru 28 a gaban babbar kotu da ke birnin na Christchurch a yau Asabar, wadda ta bada umarnin a ci gaba da tsare shi, zuwa 5 ga watan Afrilu, lokacin zamanta na biyu a kan ta’addancin da yayi.

Harin ta’addancin na ranar Juma’a dai ya sa Fira Ministar New Zealand Jacinda Ardern shan alwashin sake tsaurara dokokin mallakar bindiga a kasar, tun bayan makamancin matakin da gwamnatin kasar ta taba dauka a shekarar 1992, lokacin da wani dan bindiga ya hallaka mutane 13 ta hanyar bude musu wuta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.