Isa ga babban shafi
Amurka - Afghanistan

Akwai yiwuwar harin ta'addanci nan da sa'o'i 24-36 a Afganistan- Amurka

Kwamandojin sojin Amurka sun yi ittifakin akwai yiwuwar sake kai wani harin ta’addanci makamancin wanda aka kai  a filin jirgin  saman Kabul a cikin sa’o’i 24 zuwa 36 masu zuwa.

 Joe Biden, shugaban Amurka.
Joe Biden, shugaban Amurka. REUTERS - LEAH MILLIS
Talla

Bayan da ya samu bayanai daga tawagarsa ta tsaron kasa, shugaba Joe Biden ya fada a wata sanarwa cewa harin jirgi mara matuki a kan kungiyar Khorasan ta IS da ta dauki alhakin mummunan harin Kabul ba shine na karshe ba.

Biden ya ce yanayin da ake ciki a halin yanzu yana da matukar hadari, kuma har yanzu akwai barazanar hare haren ta’addanci a filin tashi da saukar jiragen sama na Kabul, yana mai cewa kwamandojinsa sun shaida masa yiwuwar hakan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.