Isa ga babban shafi

'Yan sandan Finland sun saki jagoran Biafra sa'o'i bayan kama shi

Jami’an ‘yan sandan kasar Finland sun saki Simon Ekpa fitacccen dan awaren da ke fafutukar neman kafa kasar Biafra a Najeriya, sa’o’i bayan kama shi da suka yi tare da yi masa jerin tambayoyi.

'Yan sandan kasar Finland yayin tafiya da Simon Ekpa domin amsa tambayoyi.
'Yan sandan kasar Finland yayin tafiya da Simon Ekpa domin amsa tambayoyi. © Premium Times
Talla

A dai ranar Alhamis din da ta gabata jami’an tsaron kasar ta Finland suka kai samame gidan Ekpa tare da cafke shi, wanda ya dade yana ikirarin goyon bayan Nnamdi Kanu, shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra ta IPOB da gwamnatin Najeriya ta haramta.

A ranar 15 ga watan Fabrairu Jakadiyar Finland a Najeriya, Leena Pylvanainen, ta bayyana rashin jin dadinta kan umarnin da Simon Ekpa ya baiwa dimbin mabiyansa na su hana gudanar zabukan kasar da suke tafe.

Tun a wacccan lokaci ne kuma, Pylvanainen ya ce jami'an tsaro a kaarsa Finland suka fara tuntubar juna dangane da matakin da za su dauka kan Ekpa.

A halin da ake ciki dai, an saki Ekpa da yammacin ranar Alhamis bayan da ‘yan sanda suka kama shi isa zarginsa da aikata wani laifi da ba a bayyana ba a Finland.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.