Kotu ta wanke Air France da Airbus daga zargin sakacin da ya kashe mutane 228
Shekaru goma sha hudu bayan hadarin Rio-Paris wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 228, alkalan Faransa sun wanke Airbus da Air France a yau litinin, hukuncin da ya harzuka dangin wadanda abin ya shafa.Kotun hukunta manyan laifuka ta Paris ta wanke kamfanonin biyu daga matakin aikata laifuka.
Wallafawa ranar:
Kotun ta yanke hukuncin ne a wani dakin shari’a cike da ‘yan uwan wadanda abin ya shafa, ma’aikatan jiragen Air France da Airbus da ‘yan jarida. Lokacin da aka sanar da sakin, wasu wakilan kungiyoyin farar hula suka mike tsaye, cike da mamaki, kamar za su bar dakin, kafin su sake zama a lokacin da shugaban ya fara jawabi a bangaren farar hula.
Dangane da haka, kotun ta yanke hukuncin cewa "kuskure" na kamfanonin ya haifar da "asara da dama.
Kotun ta dage batun tantance diyya zuwa zaman sauraren karar ranar 4 ga watan Satumba na wannan shekara.
"Mun yi tsammanin za a yanke hukunci ba tare da son kai ba, ba haka lamarin yake ba. Mun ji kunya, "in ji Danièle Lamy, shugaban kungiyar Entraide et Solidarité AF447. "Duk abin da ya rage na wadannan shekaru 14 da ake jira shi ne yanke kauna, firgici da fushi".
Air France "ya lura da hukuncin", a cewar sanarwar manema labarai. "Kamfanin zai ci gaba da tunawa da wadanda suka mutu a wannan mummunan hatsarin kuma yana nuna juyayi ga dukan 'yan uwansu.
Kamfanin Airbus ya yi la'akari da cewa wannan shawarar ta kasance "dai dai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu