Isa ga babban shafi
Wasanni

'Yan wasan Najeriya basu da kwarewar zuwa Rasha - Eguavoen

Tsohon mai horar da tawagar kwallon kafa ta Najeriya Super Eagles, Augustine Eguavon, ya ce ‘yan wasan da mai horar da tawagar na yanzu Gernot Rohr ya zaba domin halartar gasar cin kofin duniya a Rasha, basu da kwarewar da ake bukata.

Mai horar da tawagar kwalon kafa ta Najeriya, Gernot Rohr, yayin ganawa da 'yan wasansa, bayan kammala wasan sada zumunci da Ingila a London.
Mai horar da tawagar kwalon kafa ta Najeriya, Gernot Rohr, yayin ganawa da 'yan wasansa, bayan kammala wasan sada zumunci da Ingila a London. AFP PHOTO/Ian KINGTON
Talla

Eguavoen ya yi tsokacin ne, a dai dai lokacin da tawagar ta Super Eagles ke fafata wasannin sada zumunci, na baya bayan nan shi ne wanda ta buga da Ingila ranar Asabar a filin wasa na Wembley, ta kuma yi rashin nasara da 2-1.

Najeriya wadda ke rukuni na D, mai kunshe da kasashen Argentina, Iceland da Croatia, zata buga wasan farko ne da Croatia, a ranar 16 ga watan Yuni.

Najeriya ce kasa ta farko a nahiyar Afrika da fara samun tikitin halartar gasar cin kofin duniya a Rasha, kafin ta kai kammala wasanninta na neman cancantar halartar gasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.