Isa ga babban shafi
Wasanni - Kamaru

Algeria na shirin ficewa daga gasar cin kofin Afrika tun a matakin rukuni

Tawagar Equatorial Guinea ta lallasa Algeria da kwallo 1 mai ban haushi a karawarsu ta jiya, nasarar da ta bar Algeriar mai rike da kambun gasar cike da fargabar yiwuwar iya ficewa daga gasar ta cin kofin Afrika tun daga matakin rukuni.

Algeria mai rike da kambu har zuwa yanzu maki 1 tal ta ke da shi a wasannin gasar ta cin kofin Afrika da ke gudana a Kamaru.
Algeria mai rike da kambu har zuwa yanzu maki 1 tal ta ke da shi a wasannin gasar ta cin kofin Afrika da ke gudana a Kamaru. CHARLY TRIBALLEAU AFP
Talla

Sai mintuna 20 na gab da karkare wasa ne Guinea ta zura kwallon ta hannun dam wasanta Esteban Obiang kuma Algeria ta gaza farkewa duk da bugun tazarar da ta samu ta hannun dan wasan Riyad Mahrez.

Har zuwa yanzu Algeria mai rike da kambun na gasar cin kofin Afrika na da maki 1 ne tal bayan tashi wasanta na farko babu kwallo tsakaninta da Sierra Leone, kuma matukar ta na bukatar tsallakewa zuwa mataki na gaba, dole ne ta yi nasara kan Ivory Coast.

Nasarar ta Equatorial Guinea kan Algeria ya kawo karshen wasanni 35 da kasar ta arewacin Afrika ta doka ba tare da anyi nasara akanta ba, wato dai shi ne shan kayen tawagar na farko tun bayan watan Oktoban 2018.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.