Isa ga babban shafi
Kamaru

'Yan bindiga sun sace malamin jami'a a Kamaru

Wasu 'Yan bindiga a kasar Kamaru sun yi awon gaba da wani malamin jami’a a garin Beua da ke fama da tashin hankali tare da wani ma’aikacin jami’ar guda.

Sace mahukunta ko manyan mutane a kasar ta Kamaru ba sabon abu ba ne musamman a yankin 'yan aware inda a lokuta da dama kan kai ga kashe su.
Sace mahukunta ko manyan mutane a kasar ta Kamaru ba sabon abu ba ne musamman a yankin 'yan aware inda a lokuta da dama kan kai ga kashe su. AFP
Talla

Makarantar ta sanar da cewar an sace Farfesa Charles Doumta na sashen kimiyar lafiya ne tare da George Ongey da ke aiki a sashen bincike a cikin kwanaki 9 da suka gabata.

Mataimakin shugaban jami’ar, Ngomo Horace Manga ya bayyana matakin a matsayin wani yunkuri na razana malamai da daliban jami’ar domin haifar da rudani wajen harkar bada ilimi.

Ita dai jami’ar ta Beau na dauke da dalibai akalla 12,000 a kasar ta Kamaru mai fama da rikice-rikice da ayyukan ta'addanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.