Isa ga babban shafi

Kungiyoyin ta'addanci Afrika sun hade don kalubalantar G5 Sahel

Wasu rahotanni daga Burkina Faso na nuni da cewa kungiyoyin ‘yan bindiga masu ikirarin jihadi da ke kaddamar da hare-haren ta’addanci a yankin sahel sun hade waje guda don kalubalantar matakin kasashen yankin na hada karfi don kakkabe barazanar tsaron da su ke fuskanta daga kungiyoyin.

Wasu dakarun Sojin hadaka da ke yakar ta'addanci a Burkina Faso
Wasu dakarun Sojin hadaka da ke yakar ta'addanci a Burkina Faso US Army/Richard Bumgardner
Talla

A cewar tsohon shugaban ‘yan tawayen Arewa maso gabashin kasar Mali kungiyoyin wadanda suka kunshi Ansar Dine da Front du Macina da al-Mourabitoune dama AQMI baya ga Ansarul Islam da kuma kungiyar ISIS a yankin babbar Sahara, sun hade waje guda tamkar rundunar tsaro ta G5 Sahel mai yaki da ta’addanci a yankin don ci gaba da fadada hare-harensu.

Wasu bayanan sirri sun bayyana cewa wani reshe na kungiyar Macina mai rajin taimakon musulunci a Mali ne ya tallafawa kungiyoyin ta’addanci samun damar kutsa kai Burkina Faso don gudanar da hare-haren ta’addancin karkashin jagorancin kungiyar ISIS a yankin babbar sahara (EIGS).

harin baya bayana nan da aka kai a garin Boulkessi wanda aka dora alhakin kai sa kan dakarun hadakar gungun yan ta’addan a Burkina Faso inda kungiyar Ansarul Islam ke ci gaba da tabbatar da wannan babbar barzana ta hadewar kungiyoyin a cikin kasar ta Burkina Faso.

Wasu rahotanni daga majiyoyin tsaron Burkina faso sun bayyana shakku kan yadda za a ce kungiyar Ansarul Islam kadai ta kaddamar da hare-haren baya-bayan nan da ya hallaka Sojin kasar 25.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.