Kasashen Duniya na ci gaba da kira don ganin an kawo karshen yakin Libya
Kasashen Faransa, Jamus da Italiya a jiya juma’a sun bukaci ganin an kawo karshen gumurzu tsakanin dakarun Janar Haftar da sojojin gwamnatin hadin kan Tripoli dake samun goyan bayan kasashen Duniya.
Wallafawa ranar:
Shugaban Faransa Emmanuel Macron, Uwargida Angela Merkel daga Jamus da Shugaban gwamantin Italiya Guiseppe Conte a wata sanarwa ta hadin gwuiwa sun gayyacin bangarorin dake fada da juna da su kawo karshen yakin.
Shugabanin sun bayyana cewa suna a shirye don kawo shawwarwari tareda hadin gwuiwar kungiyar kasashen Afrika ta AU da majalisar dimkin Duniya don ganin an lalubo hanyoyin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a kasar ta Libya, yayinda janar Haftar ke ci gaba da bayyana aniyar sa ta afkawa birnin Tripoli cibiyar gwamnatin hadin kan kasar .
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu