Isa ga babban shafi
Sudan

Bin Laden ya bar wasiyar kudi domin jihadi

Wasu bayanan sirri daga hukumomin Amurka sun ce jagoran kungiyar Al qa’ida Osama Bin Ladan, ya mallaki dukiya ta milyoyin daloli a kasar Sudan da ya tara tare da rubuta wasiyar ware kudaden domin taimakawa ayyukan jihadi.

Marigayi Osama Bin Laden
Marigayi Osama Bin Laden @Reuters
Talla

Hukumar tara bayanan sirrin Amurka ce ta bayyana hakan a shafinta Intanet.

An samu wasiyar ne daga cikin muhimman takardu da aka gano bayan kashe Bin Ladan a wani gidansa da yak e buya a Abbottabad na kasar Pakistan 2011.

Bin Laden ya rubuta wasiyar ne ta kudi da suka kai dala miliyan 29 cikin harshen larabci, mai dauke da sa hannun marigayin.

Sannan ya bukaci danginsa su bi umurnin shi wajen sarrafa kudaden ga ayyukan jihadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.