Qatar ta yi watsi da takunkumin da aka sanya ma ta
Kasar Qatar ta yi watsi da abin da ta kira haramtaccen takunkumin da Saudi Arabia da kawayenta suka kakaba ma ta sakamakon rashin fahimtar junan da suka samu.
Wallafawa ranar:
Ministan Harkokin Wajen Qatar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman al-Thani ya bayyana haka a yayin wata ziyarar da ya kai a kasashen Birtaniya da Faransa domin yi wa shugabani bayanin assalin abin da ke faruwa.
Ministan ya ce, babu wata kasa da ta ke da hurumin tilasta wa kasarsa manufofinta na kasashen waje, in da ya ke cewa a shirye suke su tattauna akan turba mai kyau don warware matsalar amma ba katsalandan kan harkokin kasar ba.
Saudi Arabia da Daular Larabawa da Bahrain da Masar sun janye jakadunsu daga Qatar tare da katse hulda da ita saboda zargin da su ke ma ta na goyan bayan ayyukan ta’addanci.
Daga cikin zargin har da taimaka wa kungiyar Hamas ta Falasdinawa mai gwagwarmayar neman yancin Falasdinu, zargin da Qatar ta ki amincewa da shi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu