Sojin Syria sun kai hari da makami mai guba
Hare-haren sojin Syria da makami mai guba sun hallaka akalla mutane 30 a tungar ‘yan tawaye da ke kusa da birnin Damascus a jiya Litinin, yayin da al’ummar kasar ke ci gaba da shiga tsaka mai wuya sakamakon yakin shekaru bakwai da ya daidaita kasar.
Wallafawa ranar:
Da dama daga cikin mazauna yankunan da ake gwabza yaki na korafi kan yadda lugudan-wuta ke tsananta, yayin da suke zargin sojin gwamnati da yin amfani da sinadari mai guba a yankunan da ke hannun ‘yan tawayen.
Amurka ta ce, akwai kwararan hujjoji game da amfani da sinadarin Chlorine a hare-haren da aka kadamar a ‘yan makwannin nan da suka hada da harin yankin Ghouta da ke kusa da Damascus.
Kungiyar da ke sanya ido kan hakkin bil’adama a Syria mai cibiya a Biraniya ta ce, an kai hare-haren sama da kuma na makaman atilari a gabashin Ghouta a ranar Litinin, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar fararen kimanin 30 tare da jikkata wasu gommai
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu