Isa ga babban shafi
Najeriya-Faransa

Faransa za ta bada tallafin yaki da Boko Haram a Najeriya

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi alkawarin bayar da tallafin Dalar Amurka miliyan 75 don ci gaba da yaki da kungiyar Boko Haram a Najeriya da sauran kasashen da ke makwabtaka da ita.

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa da shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya a birnin Abuja
Shugaba Emmanuel Macron na Faransa da shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya a birnin Abuja RFI hausa
Talla

Shugaba Macron ya yi alkawarin ne a yayin ganawarsa da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a fadar gwamnatin kasar da ke birnin Abuja.

Macron wanda a karon farko kenan da yake ziyartar Najeriya a matsayin shugaban kasa, ya ce, gwamnatinsa za ta kuma bai wa Najeriyan bashin kudaden da yawansu ya kai Dala miliyan 475 don inganta harkokin sufuri a jihar Legas da samar da ruwan sha mai tsafta a jihar Kano, yayin da kuma za a bunkasa gandun dajin da ke jihar Ogun.

Gabanin ziyararsa a Najeriya, shugaba Macron ya gana da shugabannin kasashen Afrika a taron da suka gudanar a Mauritania, taron da ya mayar da hankali kan sha’anin tsaro a kasashen yankin Sahel da ke fama da rikicin Boko Haram.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.