Ana fargabar mutuwar fiye da mutane dubu 1 a guguwar Mozambique
Fiye da mutane dubu guda yanzu haka ake fargabar sun rasa rayukansu, kari akan mutane 150 da aka tabbatar da mutuwarsu bayan wasu da dama da suka bace a kakkarfar guguwa mai dauke da ruwan sama da ta dirarwa kasashen Mozambique da Zimbabwe.
Wallafawa ranar:
Kakkarfar guguwar wadda aka yiwa lakabi da Idai ta faro ne tun daga Alhamis din makon jiya a birnin Beira da ke tsakiyar Mozambique kafin daga bisani ta tsallaka kasar Zimbabwe.
Shugaban kasar Mozambique Filipe Nyusi ya ce har zuwa safiyar yau adadin mutane 84 ne suka mutu amma zuwa tsakiyar ranar yau da abin ya tsananta, an akwai fargabar adadin wadanda suka mutu a Ibtila'in ya haura dubu 1.
Cikin sanarwar da shugaban ya fitar a yammacin yau Litinin ta ce fiye da mutane dubu dari yanzu haka na cikin hadarin rasa rayukansu a birnin na Beira mai yawan al'umma dubu dari biyar da 30.
Sanarwar ta ce kakkarfar guguwar wadda ta haddasa ambaliyar ruwa, yanzu haka ta rushe kashi 90 cikin 100 na gidajen birnin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu