Isa ga babban shafi
Guinea Bissau

Ana zaben shugaban kasa zagaye na biyu a Guinea-Bissau

A yau lahadi al’ummar Guinea Bissau na gudanar da zaben shugaban kasar zagaye na biyu, inda Jose Mario Vaz da kuma Nuno Gomez Nabiam ke karawa da juna.

Zabe a kasar Guinée-Bissau.
Zabe a kasar Guinée-Bissau. Liliana Henriques/RFI
Talla

An dai kafa rumfanan zaben har guda dubu 3 da 48 a sassa daban daban na kasar, domin bai wa mutane dubu 775 damar jefa kuri’unsu, a wannan kasa da ta yi kaurin suna wajen aiwatar da juye-juyen mulki wanda sau dama kan haddasa asarar rayukan jama’a.
 

Daya daga cikin ‘yan takarar wato Jose Mario wanda ya samu kashi 40 cikin dari a zagayen farko na zaben, ya zargi jami’an tsaro da tursasawa magoya bayansa, yayin da abokin hamayyasar Nuna Gomez Nabiam ya yi kira da a kwantar da hankula.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.