Isa ga babban shafi
Sudan

Al-Bashir:Kotu ta yi watsi da bukatar gwamnatin Afrika ta Kudu

Babbar Kotun Afrika ta kudu ta ki amince wa da yunkurin gwamnatin Kasar na daukaka kara bayan an same ta da laifin kin kama shugaban Sudan Omar al-Bashir a lokacin da ya ziyarci Kasar. 

Shugaban Kasar Sudan Omar al-Bashir lokacin da ya dawo daga taron Kungiyar Tarayyar Kasashen Afrika a ranar 15 ga watan Yunin daya gabata
Shugaban Kasar Sudan Omar al-Bashir lokacin da ya dawo daga taron Kungiyar Tarayyar Kasashen Afrika a ranar 15 ga watan Yunin daya gabata Reuters/路透社
Talla

A ranar laraba ne babbar Kotun ta yi watsi da bukatar gwamnatin bayan an same ta da laifin barin al-Bashir har ya fice daga Kasar ba tare da tsare shi ba duk da cewa Kotu ta baiwa gwamantin umarnin cafke shi.

To sai dai gwamantin ta ce al-Bashir na da rigar kariya, abinda ya sa ta ki kama shugaban a lokacin da ya halarci taron Kungiyar Tarayyar kasashen Afrika.

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC na neman al-Bashir ruwa a jallo sakamakon zargin sa da aikata laifukan yaki a rikicin yankin Darfur na Kasar Sudan.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.