Isa ga babban shafi
Burkina Faso

Burkina ta soke sammacin kamo Guillaume Soro

Burkina Faso ta soke shelar kamo tsohon Firaministan kasar Cote d’Ivoire Guillaume Soro kan zargin da ake ma shi na hannu cikin yunkurin juyin mulkin da dakarun da ke biyayya ga tsohon shugaban kasa Blaise Compaore suka yi a kasar.

Guillaume Soro, Shugaban Majalisar Cote d'Ivoire
Guillaume Soro, Shugaban Majalisar Cote d'Ivoire AFP PHOTO / SIA KAMBOU
Talla

Mai gabatar da kara a Burkina Alioune Zanre ne ya sanar da soke sammacin da kuma dorawa Cote d’Ivoire damar Soro wanda yanzu shi ne shugaban majalisa.

Dangantaka tsakanin Burkina Faso da Cote d’ivoire na ci gaba da tsami saboda yunkurin juyin mulkin.

Akalla mutane 11 suka mutu a yunkurin juyin mulkin wanda sojojin Burkina Faso suka murkushe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.