Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

An kubutar da yara 145 daga hannu 'yan tawaye

Hukumar kula da yara kanana ta Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da nasarar kubutar da yara kanana 145 da ‘yan tawayen Sudan ta Kudu ke koyawa aikin soja.

Ana tilastawa yara kanana shiga aikin Soji a Sudan ta Kudu
Ana tilastawa yara kanana shiga aikin Soji a Sudan ta Kudu REUTERS/Jok Solomon
Talla

A wata sanarwa da ta fitar a birnin Nairobi na kasar Kenya, Hukumar ta bayyana cewa akwai yara kanana akalla dubu 16 da ke aikin sojan dole a kasar Sudan ta kudu, domin a bana kawai an dibi sama da 800 aikin sojan, har ma da bangaren sojin kasar.

A cewar Kungiyar kula da yara ta Majalisar Dinkin Duniya an kubutar da yaran ne daga wata kungiyar mai sunan Cobra da kuma SPLA/10 dukkan su a gunduman Pibor.

Ko a bara a cewar sanarwar kananan yara 1775 aka kubutar daga aikin sojin.

Wadanan yara dai an kwace makaman da ke hannun su aka basu kayan sawa, kafin a yi masu huduba sosai a game da illar shigan su harkan soji da kananan shekaru.

Tun a shekara ta 2013 kasar Sudan ta kudu da ta ke murnar samun ‘yan ci daga Sudan ta fara yaki da ya hallaka mutane da dama wasu kuma aka tilasta masu yin hijira.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.