Aubameyang da Mahrez na takarar gwarzon Afrika
Dan wasan Borussia Dortmund dan kasar Gabon Pierre-Emerick Aubameyang na cikin ‘yan wasa biyar da hukumar kwallon CAF ta ware domin zaben gwarzon dan wasan Afrika na bana.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Sauran ‘Yan wasan sun hada da Riyad Mahrez da Islam Slimani ‘Yan kasar Algeria da ke taka kwallo a Leicester City ta Ingila. Da Sadio Mane na Senegal dan wasan kungiyar Liverpool da Mohamed Salah na Masar da ke wasa a kungiyar Roma ta Italiya.
Aubameyang ne ke rike da kambun kuma a bana ana ganin yana iya lashe kyautar. A bana Dan wasan ne na Gabon masanin raga ya lashe kyautar gwarzon dan wasan Jamus.
Kodayake akwai Mahrez da ya taimakawa Leicester City lashe kofin Firimiya tare da jefa kwallaye 17 a raga a kakar da ta gabata.
A ranar 5 ga watan Janairu ne CAF zata zabi gwarzon dan wasan na Afrika a Abuja babbar birnin Najeriya
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu