Isa ga babban shafi
Sudan

Za a dawo da mukamin Firaminista a Sudan

A yau Laraba majalisar dokokin Sudan ta kada kuri’a sake dawo da kujerar Firaminista bayan soke mukamin a shekara ta 1989 al’amarin da ya biyo bayan juyin mulkin da shugaba Omar al-Bashir ya jagoranta.

Shugaban kasar Sudan Oumar al-Bashir.
Shugaban kasar Sudan Oumar al-Bashir. REUTERS/Siphiwe Sibeko
Talla

Matakin dawo da kujerar Firaminista a kasar zai yi tasiri ga sauye-sauye da gwamnatin al-Bashir ke shirin aiwatar wa bayan cimma yarjejeniyar hadin kan kasa tsakanin gwamnatinsa da kungiyoyin ‘yan adawa.

Shugaba al-Bashir ya soke kujerar Firaministan ne bayan jagoranta juyin mulki da ya kifar da Gwamnatin Sadiq al-Mahdi da taimakon sirikinsa, Hassan al-Turabi jogoran muslunci na wanann lokaci a kasar.

A watan Oktober, bayan shafe sama da shekaru 25 kan karagar mulki, al-Bashir ya amince da yarjejeniyar zaman lafiya a kasar da aka jimma ana zub da jini da kuma farfado da tatatlin arzikin kasar.

A ranar 10 a watan oktoba, shugaban ya gabatar sabon kudirin tsarin mulkin kasa, wanda ya samu amincewar ‘yan majalissu 387 daga cikin 425.

Sabon kudin tsarin mulkin a yanzu zai bai wa sabon Firaministan karfin ikon mulki.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.