Isa ga babban shafi
Sudan

Al-Bashir ya ce sai Shekarar 2020 zai sauka daga Mulki

Shugaban Sudan Umar Hasan Albashir ya ce zai sauka daga mukaminsa amma sai a shekara ta 2020 idan Allah ya kai mu wanda shi ne karshen wa’adin mulkin da yake kai a yanzu.

Shugaban kasar Sudan Omar Hassan al-Bashir
Shugaban kasar Sudan Omar Hassan al-Bashir Reuters/Mohamed Nureldin Abdallah
Talla

Albashir dai ya dare kan karagar mulkin kasar tun 1989 ta hanyar juyin mulki. Yanzu haka kotun duniya na nemansa domin hukunta shi a game da zargin aikata laifufukan yaki a yankin Darfur da cin zarafin bil’adama.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane dubu 300 aka kashe a yakin Sudan, kana sama da miliyan biyu da rabi sun kauracewa gidajensu saboda rashin kwanciyar hankali, alkallumar da ya zarce wanda Khartoum ta fitar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.