Taron gidauniya zuwa yan gudun hijira na Sudan ta Kudu
A taron gidauniya da ya gudana a kasar Uganda, manyan kasashen Duniya sun maida hankali zuwa hanyoyin kawo karshen kwarrarar yan gudun hijira da aka kiyasta yawan su zuwa milyan daya .
Wallafawa ranar:
Taron da ya samu halartar Sakatary Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres da Shugabanin kungiyoyin kasashen Duniya sun dau alkawalin ware kudi milyan 358 na dalla a matsayin taimako zuwa yan gudun hijira da akasarin su rikicin Sudan ta kudu ya tilasta masu baro gidajen su.
Antonio Guterres ya yi kira zuwa kungiyoyin dake fada da juna da cewa kawo karshen wannan rikici na zubar da jinni ne kawai zai kawo karshen kwarrarar yan gudun hijira daga yankunan su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu