Kenya:Raila Odinga ya rantsar da Kansa
Rahotanni daga birnin Nairobi na cewa madugun adawa kasar Kenya, Raila Odinga ya rantsar da kansa a matsayin sabon shugaban kasa a gaban dafifin jama’a.
Wallafawa ranar:
Wannan kasaitaccen bikin rantsuwa anyi shine a fitaccen dandalin tunawa da Uhuru da ke Nairobi, kuma duka-duka a cikin minti 10 aka kammala.
Magoya bayan Odinga dai sun ce shine wanda ya lashe zaben kasar ba shugaba mai ci Uhuru Kenyata ba.
A watan Agustan shekarar da ta gabata Kotun kolin kasar ta soke zaben da ya bai wa Shugaba mai-ci Uhuru Kenyatta nasara kan dalilan magudi.
Sai dai kuma da aka sake yin zaben zagaye na biyu wanda ‘yan adawa suka kauracewa Kenyatta ya sake samun nasara a watan Nuwamba 2017.
Daga cikin dalilan kauracewa zaben da ‘yan adawan suka gabatar akwai zargin kin aiwatar da wasu sauye-sauye a hukumar zaben kasar.
A yanzu dai Raila Odinga na nuna babu gudu ba ja da baya a game da matakin da ya dauka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu