Isa ga babban shafi
Togo

'Yan adawa na zaman sulhu da gwamnatin Togo a yau

Bayan share tsawon watanni 6 ana takun-saka tsakanin gwamnati da kuma ‘yan adawa a kasar Togo, a yau litinin bangarorin biyu za su fara tattaunawar sulhu tare da shiga tsakanin wasu kasashe na yammacin Afirka.

Zauren da aka bude taron sulhunta rikicin siyasar Togo tsakanin gwamnati da 'yan adawa a birnin Lome.
Zauren da aka bude taron sulhunta rikicin siyasar Togo tsakanin gwamnati da 'yan adawa a birnin Lome. RFIHAUSA/Abdoulaye Issa
Talla

Tuni shugaban Ghana Nana Akufo-Addo, ya isa birnin Lome fadar gwamnatin kasar ta Togo domin jagorantar bikin fara tattaunawar, in da kowanne daga cikin bangarorin biyu zai aike da wakilai 7 a wannan tattaunawa da za ta share fiye da tsawon kwanaki 10.

Majalisar Dinkin Duniya da Kungiyar Tarayyar Turai da jakadun Jamus da Faransa da Amurka sun yi madalla da yunkurin zaman tattaunawar ta yau, in da suka bukaci bangarorin da su cimma matsaya.

An dai gudanar da jerin zanga-zangar adawa da shugaba Faure Gnassingbe don ganin ya sauka daga kujerarsa tare da samar da dokar takaita wa’adin shugabancin kasar.

Tun a shekarar 2005, shugaba Gnassingbe ya dare kan karaga bayan ya gaji mahaifinsa, Janar Gnassingbe Eyadema da ya shugabanci kasar tsawon shekaru 38 bayan ya yi juyin mulki a 1967.

Da dama daga cikin al’ummar kasar na fatan cimma matsaya tsakanin ‘yan adawa da gwamnatin a tattaunawar ta yau don ganin an samar wa karamar kasar makoma ta gari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.