WHO ta koka da matakan Afrika na tunkarar Coronavirus
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana damuwa kan shirin da kasashen Afirka ke da shi wajen fuskantar coronavirus ko kuma COVID-19 idan an samu barkewar ta a kasar.
Wallafawa ranar:
Shugaban Hukumar Tedros Adhanom Gebreyesus ya bukaci kasashen Afirka da su hada kan su wajen daukar kwararan matakan tinkarar cutar.
Yayin ganawa da ministocin lafiyar Afirka a Addis Ababa, Gebreyesus ya ce su na cikin fargaba dangane da samun cutar a Afirka lura da irin matsalolin da suka dabaibaye harkokin kula da lafiyar jama’a a nahiyar.
Ya zuwa yanzu cutar ta hallaka mutane sama da 2,200 a China bayan ta kama mutane sama da 75,500, yayin da aka samu mutane 1,150 da suka kamu da cutar a wajen China.
Kasar Masar ce kasa daya tilo da ta sanar da samun cutar a Afirka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu