Isa ga babban shafi
Afirka ta Kudu

ANC na daf da samun sakamakon zabe mafi muni tun bayan zamanin wariya

Jam’iyyar ANC mai mulkin Afrika ta Kudu na daf da samun  sakamako mafi muni  tun bayan  mulkin wariya na apartheid, inda ake ganin goyon bayanta zai yi kasa da kaso 50 a zaben kananan hukumomi.

Cyril Ramaphosa, shugaban Afrika ta Kudu.
Cyril Ramaphosa, shugaban Afrika ta Kudu. Sumaya HISHAM POOL/AFP/File
Talla

A yayin da kaso 30 na rumfunan zabe suka sanar da sakamako biyo bayan zaben da aka gudanar  a Litinin, Jam’iyyar African National Congress, ANC ta samu kaso 46 na  kuri’un da aka kada, kamar yadda alkaluman hukumar zaben kasar  suka nuna.

An yi yekuwa ga masu zabe  da su fito su kada kuri’a zaben wadanda za su wakilce su a matakin kananan hukumomi da zumar kula da mahimman batutuwa da suka hada da wutar lantarki,  samar da gidaje ruwan sha da tsaftar muhali.

Afrika ta Kudu ta shafe shekaru tana fuskantar ha’inci a game da yadda ake gudanar da al’amuranta, a  yayin da jiga jigan jam’iyyar ANC mai mulki da suka hada da tsohon shugaba Jacob Zuma  ke fuskantar tuhumar rashawa, kana rashin aikin yi ya kai  sama da kaso 34 a kasar.

Har zuwa shekarar 2016, jam’iyyar ANC ce ta yi ta lashe kaso 60  na dukkannin kuri’un da ake kadawa tun da aka fara bai wa dukkan jinsina damar yin zabe a kasar, a a shakarar 1994, lokacin da aka rantsar da Nelson mandela a matsayin shugaban kasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.