Isa ga babban shafi

Jam'iyyar ANC ta Ramaphosa ta rasa rinjaye a zaben kasar

Jam’iyyar Shugaban kasar Afrika ta Kudu ta sha kayi a zaben wakilan hukumomin. Wannan dai ne karo na farko da jam’iyar  marigayi Nelson Mandela ta fuskanci irin wannan  kaye ,tareda samun kasar da kashi 50 cikin dari na sakamakon zaben da ya gudana.

Magoya bayan jam'iyyar ANC ta shugaba Ramaphosa
Magoya bayan jam'iyyar ANC ta shugaba Ramaphosa AFP - PHILL MAGAKOE
Talla

Jam’iyyar ta rasa shida daga cikin manyan biranen takwas da ake da su a kasar.Wannan sakamakon zabe kan iya kai jam'iyyar ga rasa wasu daga cikin manyan kujeru tareda kai shugaban kasar Cyril Ramaphosa ga rasa kujerar sa a duk lokacin da ake zaben kasar.

Shugaba Ramaphosa a zaben wakilan hukumomin kasar
Shugaba Ramaphosa a zaben wakilan hukumomin kasar Michele Spatari AFP/Archivos

Da samun wannan labari,kwamityn zartawa na jam’iyyar ANC  ya kira taron gaggawa da wakilan jam'iyyar da nufin tattaunawa dangane da makomar jam’iyyar a wannan lokaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.