Isa ga babban shafi

Sojan Faransa na 53 ya mutu a yankin Gao na kasar Mali

Wani sojan Faransa ya rasa ran sa a jiya asabar a kasar Mali bayan wani harin da manyan bindigogi da aka kai bariqin sojojin Barkhane dake garin Gao. Sanarwar da fadar Shugaban Faransa ta Elysee ta bayar na nuna cewa Shugaban kasar Emmanuel Macron cikin kaduwa ya bayyana jimamen sa tareda isar da ta’aziya ga iyalan mammacin  Birgaidiya Alexandre Martin dake aiki da rundunar artillery ta 54.

Dakarun Barkhane a birnin Gao na kasar Mali
Dakarun Barkhane a birnin Gao na kasar Mali © RFI Mandenkan / Sory Ibrahim
Talla

Gwamnatin Faransa ta bayyana cewa babu gudu ba ja da baya za ta ci gaba da yakin da take da yan ta’adda tare da goyan bayan kawayan ta a Sahel.

Wani sojan Faransa  a garin Gao
Wani sojan Faransa a garin Gao Thomas COEX AFP/File

Da misalign karfe  biyar na yammacin jiya ne  aka yi ta jin harbi da manyan makamai zuwa bariqin sojojin barkhane dake yankin na Gao a cewar mai magana da yahun rundunar tsaron Faransa Kanal Pascal Ianni.

Sojan Barkhane na kasar Faransa a birnin Gao
Sojan Barkhane na kasar Faransa a birnin Gao © RFI/Franck Alexandre

Kanal Pascal ya karasa da cewa nan take,aka tayar da jirage masu saukar ungulu  da nufin murkushe maharani,nasar da suka samu ba tare da bata lokaci ba.Wannan dai ne sojan Faransa na 53 dake rasa ran sa a kasar ta Mali tun bayan shigar Faransa yakin a shekara ta 2013

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.