Isa ga babban shafi
Equatorial Guinea

Guinea ta biya diyyar wadanda suka mutu saboda fashewar bama-bamai a 2021

Gwamnatin Equatorial Guinea ta biya diyya ga iyalai 84 na mutane fiye da 100 da suka mutu sakamakon fashewar bama-bamai a wani sansanin sojin kasar a shekarar bara.

Yadda fashewar bama-bamai ya rusa gine-gine a garin Bata na kasar Equatorial Guinea.
Yadda fashewar bama-bamai ya rusa gine-gine a garin Bata na kasar Equatorial Guinea. © ASONGA TV/via REUTERS TV/File Photo
Talla

Fashe-fashen har kasha 4 sun auku ne a sansanin Nkoa Ntoma da ke birnin Bata, cibiyar tattalin arzikin kasar mai arzikin mai, inda mutane 107 suka mutu, yayin da wasu 615 suka jikkata a ranar 7 ga Maris na shekarar 2021.

Bayanai sun ce gwamnatin Equatorial Guinea ta ware CFA miliyan 700 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 1.1 ne don biyan diyya ga wadanda abin ya shafa, inda iyalan wadanda suka mutu suka samu CFA miliyan takwas kowannensu yayin da wadanda suka jikkata suka  samu CFA miliyan 4-4.

An yi taron mika diyyar ne a ranakun Juma’a da kuma Asabar karkashin jagorancin Teodoro Nguema Obiang Mangue, mataimakin shugaban kasa kuma dan shugaban kasar da ya dade yana mulki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.