Isa ga babban shafi

E-Guinea ta yi barazanar korar jakadan Faransa daga kasar

Mataimakin shugaban Equatorial Guinea, Teodoro Nguema Obiang Mangue, ya yi barazarar korar jakadan Faransa daga kasar a daidai lokacin da alaka ke dada tsami tsakanin kasashen biyu, daga lokacin da aka gurfanar da mataimakin shugaban gaban kotun Paris saboda zargin rashawa.

Dan shugaban Equatorial Guinea Teodoro Obiang Nguema,
Dan shugaban Equatorial Guinea Teodoro Obiang Nguema, AFP/File
Talla

A shekarar da ta gabata ne dai kotun daukaka kara a Faransa ta tabbatar da hukuncin daurin talata na shekaru uku da aka yanke wa mataimakin shugaban kasar ta Guinea bayan samun shi da rashawa da kuma boye makudan kudade a kasar.

Wannan hukunci dai ya share fagen kwace wani katafaren gida mai fadin murabba’in mita dubu da aka kiyarsta cewa zai kai Euro milyan 107 a birnin Paris.

A shafinsa na Twiitter, Obiang ya ce matukar aka fitar da jami’an diflomasiyar Guinea daga cikin wannan gida, to lalle kuwa zai bayar da umurnin tasa keyar jakadan na Faransa a cikin sa’o’I 24.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.