Isa ga babban shafi

Mutane da dama sun mutu yayin wata zanga-zanga a Saliyo

Jami’an ‘yan sanda biyu ne aka kashe a kasar Saliyo, bayan wata zanga-zangar nuna adawa da matsalar tattalin arziki da ta barke tsakanin jami’an tsaro da matasa tare da neman shugaban kasar ya yi murabus.

'Yan kasar dai na kokawa kan matsin tattalin arzikin da suke fama da shi
'Yan kasar dai na kokawa kan matsin tattalin arzikin da suke fama da shi via REUTERS - PICTURE OBTAINED BY REUTERS
Talla

Hakan ta sanya mataimakin shugaban kasar Mohamed Juldeh Jalloh ya sanar da kafa dokar ta-baci a fadin kasar yayin da ya fitar da sanarwar cewa an kashe wasu daga cikin masu zanga-zangar, ciki har da wasu jami’an tsaro.

hukumomin tsaron kasar sun ce an kama masu zanga-zangar da dama, yayin da fusatattun matasa da dama suka shaidawa AFP cewa ‘yan sand ana harba musu harsasai.

Wani ma'aikacin lafiya a wani asibiti da ke Freetown ya ce mutane da dama sun jikkata.

A yankin Kissy da ke gabashin birnin, masu zanga-zangar sun jefi jami'an tsaro da duwatsu da sanduna, bayan da suka harba musu hayaki mai sa hawaye.

An dai ji masu zanga-zangar suna rera taken "Bio must go" wato suna nufin shugaba Julius Maada Bio, wanda a halin yanzu yake kasar Burtaniya a wata ziyarar sirri sai ya sauka daga shugabancin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.