An samu nasarar kawar da cutar Marburg a Equatorial Guinea - WHO
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta ce an kawo karshen cutar Marburg a Equatorial Guinea, bayan da aka cika kwanaki 42 ba tare da an samu wanda ya harbu da cutar da ake yiwa lakabi da kanwar Ebola.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Masana kiwon lafiya sun bayyana cutar a matsayin babbar barazana da ke sanyawa dan adam tsananin zazzabi, zubar jinni da kuma yin illa ga sassan jikin mutum.
A ranar 13 ga watan Fabrairu ne, aka bayyana cutar a matsayin annoba a Equatorial Guinea, karon farko da kasar ta taba irin wannan cuta a kasar da ke Tsakiya maso Yammacin Afirka.
Mutum 17 aka tabbatar sun harbu da cutar, yayin da 12 suka mutu. Amma WHO ta ce dukkanin mutum 23 da aka gano sun mutu.
Sanarwar da WHO ta fitar, ta yabawa jami’an lafiya da sauran kungiyoyi na hadin gwiwa da suka taimaka wajen kawar da cutar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu