Isa ga babban shafi

Aljeriya ta tisa keyar yan ci ranin kasashen Afrika sama da dubu 9 a jamhuriyar Nijer

Rahoton wasu hukumommin majalisar dinkin duniya biyu ya ce Algeria  ta tisa keyar  bakin-haure ‘yan Afrika sama da dubu 9 daga iyakarta zuwa Jamhuriyar Nijar, lamarin da ya haddasa mummunar matsalar jinkai. 

Les migrants sont véhiculés jusqu'à Bordj Badji Mokhtar. Ensuite, ils doivent marcher jusqu'à la frontière malienne.
Les migrants sont véhiculés jusqu'à Bordj Badji Mokhtar. Ensuite, ils doivent marcher jusqu'à la frontière malienne. Google maps
Talla

A cikin rahoton, hukumar kula da  ayyukan jinkai ta OCHA da ta kula da bakin haure sun ce tun daga farkon wannan shekarar ce mahukuntan Algeria suka kori wannan adadi na bakin haure, inda suka makale a wani gari da ake kira Assamaka da ke jihar Agadez. 

Mahukuntan Nijar sun yi wa sama da mutane dubu 9 da ke shigowa rajista, cikinsu maza dubu 8 da dari 8 da 28, mata 161, yara maza 152 da yara  mata 51 tun dvaga watan Janairu. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.