Isa ga babban shafi

ECOWAS ta yi watsi da tayin mika mulki bayan shekaru 3 da sojojin Nijar suka yi

Kungiyar Raya Tattallin Arzikin Kasashen Afrika ta Yamma ECOWAS ta yi wasti da tayin wa'adin shekaru 3 na mika mulki ga farar hula da gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta yi.

Kwamishinan harkokin siyasa, zaman lafiya da tsaro na kungiyar ECOWAS, Abdel-Fatau Musah.
Kwamishinan harkokin siyasa, zaman lafiya da tsaro na kungiyar ECOWAS, Abdel-Fatau Musah. REUTERS - FRANCIS KOKOROKO
Talla

Kwamishinan Harkokin Siyasa, Zaman Lafiya da Tsaro na kungiyar, Abdel-Fatau Musah ne ya sanar da haka a ganawarsa da wata kafar yada labarai ta kasa-da-kasa.

A ranar Asabar, shugaban gwamnatin sojin Nijar Janar Abdourahmane Tchiani ya sanar da aniyar sojojin ta mika mulki ga farar hula a cikin shekaru 3 a wani jawabin da ya yi ga al'ummar kasar ta kafar talabijin, lamarin da ya haddasa cece-kuce a ciki da wajen kasar.

Shugaban gwamnatin sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani ya ce sai nan da shekaru uku masu zwua za su mika mulki ga farar hula.
Shugaban gwamnatin sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani ya ce sai nan da shekaru uku masu zwua za su mika mulki ga farar hula. AP
A makon da ya gabata ne, tsohon shugaban Najeriya, Janar Abdulsalami Abubakar ya jagoranci tawagar kungiyar ECOWAS zuwa Jamhuriyar Nijar a wani yunkuri na lalubo masalaha ta hanyar diflomasiyya.

Tawagar ta hadu da firaminista Ali Lamine Zeine, wanda ya tarbe su a filin tashi da saukar jiragen sama, kana ya jagorance su zuwa fadar shugaban kasa.

Bayan ganawa da shugaban gwamnatin sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, tawagar ta ECOWAS ta tattauna da hambararren shugaban kasar, Bazoum Mohamed wanda bayanai ke nuni da cewa yana cikin koshin lafiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.