Isa ga babban shafi
Canada-Burkina

Canada ta janye tallafin da ta ke ba Burkina Faso

Gwamnatin kasar Canada ta fitar da sanarwar janye tallafin taimako da ta ke ba kasar Burkina Faso saboda Sojoji sun kwace mulki bayan ‘Yan adawa sun tursasawa Blaise Compaore yin murabus. Ofishin Ministan kula da bayar da tallafi ga kasashen waje yace Canada ta janye tallafin da ta ke ba Burkian Faso saboda halin da kasar ke ciki a halin yanzu.

Masu Zanga-zanga a Ouagadougou, Kasar Burkina Faso
Masu Zanga-zanga a Ouagadougou, Kasar Burkina Faso REUTERS/Joe Penney
Talla

Kasar Canada dai na daya daga cikin kasashen da ke ba kasar Burkina Faso tallafi gwajen bunkasa ayyukan noma da masana’antu da kiwon lafiya da kuma kare hakkin Mata.

Canada tace zata ci gaba da Burkian tallafi idan kasar ta dawo a turbar dimukuradiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.