Isa ga babban shafi
Vatican

Paparoma ya koka da hare haren Nukiliyan Hiroshima da Nagasaki

Paparoma Francis yace har yanzu hare hare bama baman Nukiliyan da aka kai a biranen Hiroshima da Nagasaki na Japan, suna ci gaba da jefa fargaba da tayar da hankulan jama’a, shekaru 70 bayan faruwar lamarin.

Wata alama ta hana yaduwar makaman Nukiliya
Wata alama ta hana yaduwar makaman Nukiliya REUTERS/Danish Siddiqui
Talla

Paparoman, dake magana yau Lahadi, ranar da ake cika shekaru 70 da kai hare haren, ya nemi a haramta makaman Nukuliya, da ma sauran makaman kare dangi a fadin duniya.
Ranar 6 ga watan Augustan shekarar 1945, wani jirgin saman yakin Amurka ya jefa bom a birnin Hiroshima, ya kashe kimanin mutane dubui 140, lokacin da ake gab da kawo karshen yakin duniya na 2.
Kwanaki 3 bayan nan ranar 9 ga wata aka sake jefa wani makamin mai guba a birnin of Nagasaki, da shi kuma ya hallaka fiye da mutane dubu 70, rana 15 ga wata kuma Japan ya mika wuya a yakin.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.