Isa ga babban shafi
Venezuela

An harbe wani dan takara a Venezuela

A yayin da ake gudanar da zaben ‘yan majalisu a Venezuela mai fama da rikici da matsalolin tattalin arziki, rahotanni sun ce an kashe daya daga cikin ‘yan takarar dan majalisa.

'Yan sanda na arangama da masu zanga-zanga a Caracas
'Yan sanda na arangama da masu zanga-zanga a Caracas REUTERS/Carlos Garcia Rawlins
Talla

Jose Felix Pineda, wanda lauya ne kuma daya daga cikin wadanda ke gwagwarmayar sake rubuta kundin tsarin mulki, an kashe shi ne a gidansa da ke garin Bolivar kafin soma kada kuri’a.

Ana zaben ne dai cikin yanayi na fargaba da tashin hankali a Venezuela inda wasu rahotanni suka ce an kashe shugaban matasa ‘yan adawa a wani gangani adawa da zaben da ake gudanarwa a yau Lahadi.

An shafe kwanaki ana zanga-zangar kin jinin gwamnatin Nicolas Maduro, inda mutane sama da 100 suka mutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.