Isa ga babban shafi
amurka-venezuela

Trump na nazarin daukan matakin soji kan Venezuela

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce, yana duba yiwuwar daukan matakin soji a matsayin martani game da rikicin Venezuela da ya ki ci ya ki cinyewa.

Wasu Jami'an sojin Venezuela a yayin arangama da masu zanga-zangar adawa da gwamnati.
Wasu Jami'an sojin Venezuela a yayin arangama da masu zanga-zangar adawa da gwamnati. REUTERS/Ueslei Marcelino
Talla

Sai dai tuni, gwamnatin Venezuela ta gaggauta yin watsi da yunkurin Trump da ta bayyana a matsayin hauka.

Amurka ta kakaba takunkumai kan shugaba Nicolas Maduro da wasu aminansa sakamakon matakin da ya ke dauka na murkushe ‘yan adawar Venezuela .

Kimaniun watanni hudu kenan da ake fama da rikicin siyasa a Venezuela , in da kusan mutane 130 suka rasa rayukansu sakamakon tarzoma tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar adawa da gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.