Akalla Mutane 150 sun mutu a kogi a yayin tserewa harin Boko Haram
A Jahar Yobe da ke tarayyar Najeriya, akalla mutane 150 ne suka hallaka a kogi, a lokacin da suke kokarin tserewa daga harin ‘yan Boko Haram a wani kauye da ke jihar ta Yobe.
Wallafawa ranar:
Lamarin dai ya faru ne a wani kauye mai suna Kukuwa-Gari, kamar dai yadda wasu da suka tsira da rayukansu suka shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa.
Al’ummar yankin arewa maso gabashin Najeriya na ci gaba da fuskantar munanan hare haren mayakan kungiyar Boko Haram.
Yanzu haka dai rundunar Sojin kasar ta sanar da kaddamar da hare hare ta sama akan mayakan na Boko Haram dake labe a dajin sambisa.
Tuni dai Shugaban Kasar Muhammadu Buhari ya bukaci sabbin Manyan hafsoshin tsaron Kasar da su kawo karshen ta’addancin Kungiyar nan da watanni uku masu zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu