Ya kamata gwamnatin Najeriya ta sanya takunkumi ga ‘yan fashin da ke yiwa mata fyade - UNICEF
Wakiliyar Asusun Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya UNICEF a Najeriya, Cristian Munduate, ta bukaci Gwamnatin kasar da ta yi amfani da dokokin da suka dace domin gurfanar da ‘yan fashin da suka aikata ta’asar cin zarafin Bil Adama.
Wallafawa ranar:
Cristian ta yi wannan kiran ne a yayin wani taron tattaunawa da manema labarai na shirye-shiryen bikin ranar jin kai ta duniya a birnin Maiduguri.
UNICEF ya yi nuni da cewa, abu ne da ba za a amince da shi ba a ce gwamnatoci ba su dauki tsattsauran mataki ba a kan wadanda suka sace daliban makaranta, da kashe mata da malamai, da kuma yi wa kananan yara mata fyade.
Ta yi kira da a karfafa tsarin shari’a yadda ya kamata, ta kuma yi gargadin a daina wannan aika-aika ta yadda yara za su iya zuwa makarantu ba tare da fargabar sace ko yi musu fyade ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu