Isa ga babban shafi

Nigeria: Makarantu 723 a Najeriya na rufe a jihohi 9 sakamakon rashin tsaro-UNICEF

Asusun kula da kananan yara UNICEF na MDD ya bayyana cewa akalla makarantu 723 ne yanzu haka a rufe a jihohi 9 na Najeriya, a yayin da aka jibge ‘yan gudun hijira a wasu da dama daga cikin su, a sanadin rashin tsaro ko kuma matsalolin da suka da ambaliyar ruwa da suka haifar da cikas ga ayyukan karantarwa.

Wakiliyar UNICEF yayin da take jawabi
Wakiliyar UNICEF yayin da take jawabi © Arquivo pessoal
Talla

Alkaluman Asusun na UNICEF  sun nuna cewa jihohin da wannan iftila’i ya shafa sun hada da Adamawa da Benue da Borno da Imo da katsina da Kebbi da Sokoto da Yobe da kuma Zamfara.

Asusun ya kara da cewa matsalar tsaro itace babbar matsalar da tafi shafar harkokin  karatun wadda ya kai ga rufe su har na tsawon lokaci.

Majalisar  dinkin duniya dai ta bayyana cewa cikakken zaman lafiya baya samuwa indai babu ingantaccen tsaro a cikin al’uma, don haka ya zama wajibi a hada karfi da karfe wajen tabbatar da tsaron a fadin kasar don samun bunkasar ilimi.

Matsalar rashin tsaron ta kasance tamkar tsinkewar wata muhimmiyar jijiya ce wacce in babu ita to dukkanin lamura sun dagule, Wanda hakan ya sanya baya ga rashin samun damar bude makarantu matsalar ta haifar da durkushewar harkokin tattalin arziki a sassan kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.